Shattiman na magazu ya yi wannan kiran ne, a lokacin da ake tattaunawa kai tsaye da shi akan manufar kungiyar matasan zamfara ta Tsakkiya, tare da amsa wasu daga cikin tambayin da sunka shafi kungiyar.
A cewarsa "Kungiyar matasan zamfara ta Tsakkiya zata yi bakin kokarinta wajen biya matasa kudaden Makaranta tare da ba su scholarship. Haka zalika za ta bullo da shiraruwa da za su taimaki rayuwar matasan.
"Daga nan ya yi kira ga shugabanni, 'yan siyasa da kuma masu hannu da shuninmu da su dauki dabi'ar tallafawa matasa su yi karatu. Musamman Ganin cewa akwai matasa da dama da ke son yin karatu, amma Dan abunda bai taka kara ya karya ba ya hanasu yinsa" a cewarsa.

