'YAN SIYASA NA CIGABA DA RIBIBIN BAIWA MALAM WAKKALA GUDUNMAWAWI DA ZUMNAR KARFAFA SHI DA GOYA MASA BAYA DOMIN NEMAN KUJERAR GWAMNAN ZAMFARA A 2019 - MAIBIREDI TV

MAIBIREDI TV

Na kirkiri wannan blog ne, domin kawo labarai na ciki da wajen Najeriya dama rubutu akan ababen da ke faruwa a jahar Zamfara.

Breaking

Home Top Ad

Responsive Ads Here

Post Top Ad

Responsive Ads Here

Thursday, 28 June 2018

'YAN SIYASA NA CIGABA DA RIBIBIN BAIWA MALAM WAKKALA GUDUNMAWAWI DA ZUMNAR KARFAFA SHI DA GOYA MASA BAYA DOMIN NEMAN KUJERAR GWAMNAN ZAMFARA A 2019



Yan siyasa a lungu da Sako na jahar Zamfara suna cigaba da ribibin Baiwa Malam Ibrahim Wakkala Muhammad Liman (Sarkin Malaman Gusau ) Kuma mataimakin gwamnan jahar Zamfara, gudunmawowin motoci, Babura da sauran kayayyankin yakin neman zabensa.

Na baya-bayan nan shi ne Alhaji Abubakar Jatau Kanoma ( Sarkin Bauran Maru) Wanda a cikin Daren yau Alhamis 28-6-2018 ya bada gudunmawar mota 406 mai lamination, Riguna 700, Hulluna 700 da Posta kwafi 5000.

Sarkin Bauran dai Can baya ma ya baiwa mataimakin gwamnan gudunmawowi domin mara masa baya tare da karfafa shi domin neman gwamnan jahar Zamfara a 2019..

A lokacin da ya ke maida jawabi 

Maitaimakin gwamnan jahar Zamfara, ya nuna jin dadinsa Matuka da gaske da wannan kyautar, Kuma ya nuna cewa hakan ya nuna cewa akwai masu nuna soyayya Dan Allah.

Daga karshe mataimakin gwamnan ya bayyana cewa mutane irin Bauran Maru na Daga cikin dubban mutanen da ke kara masa karfin guiwa wajen neman kujerar gwamnan a 2019. 

Post Bottom Ad

Responsive Ads Here