TSORON 'YAN TA'ADDA SU YI MUNA KISAN KIYASHI YA SA MUKA YI GUDUN HIJIRA ZUWA GUSAU= DARURUWAN 'YAN GUDUN HIJIRA. - MAIBIREDI TV

MAIBIREDI TV

Na kirkiri wannan blog ne, domin kawo labarai na ciki da wajen Najeriya dama rubutu akan ababen da ke faruwa a jahar Zamfara.

Breaking

Home Top Ad

Responsive Ads Here

Post Top Ad

Responsive Ads Here

Friday, 1 June 2018

TSORON 'YAN TA'ADDA SU YI MUNA KISAN KIYASHI YA SA MUKA YI GUDUN HIJIRA ZUWA GUSAU= DARURUWAN 'YAN GUDUN HIJIRA.


Daruruwan 'yan gudun hijira Maza da mata, yara kanana da kuma tsofaffi sunka durfafo garin garin GUSAU a yau, Jumu'a. Domin gujewa wasu miyagun 'yan ta'adda da za su shigo a kauyukkansu.


'yan gudun hijrar dai sun Fito ne, Daga yankin jangeme zuwa Magami. 

Duk wani yunkuri namu na zantawa da su kamar yadda ya dace yacitura. Saboda Tsoro da ke tattare da su. Domin tashin hankali da ke tattare da zuciyoyinsu, Wanda ya sa mata da yaran cikinsu ke ta kuka.

Yanzu haka dai sun bar bayan gidan marigayi Ummaru Shinkafi da ke GRA GUSAU a yunkurinsu na neman jami'an TSARO DA ZA su raka su zuwa kauyukkansu tare da ba su kariya. Sai dai tuni Shugaban karamar Hukumar mulkin Gusau, Hon. Ibrahim Umar Tanko ya zo gunsu har ya ba su kudin shan mai. Tare da daukar matakin da ya dace, Duk dai yanzu da na ke wannan rubutun ba wani jami'in Tsaro ko jami'in Gwamnati da ya zo gunsu.

Jahar Zamfara dai ta yi kaurin suna wajen yawaitar tashe-tashen hankula daga 'yan ta'adda da ke kisa, garkuwa da mutane da ma salwantar da dukiyoyi.





Post Bottom Ad

Responsive Ads Here