Alhamdulillahi Bayan kashe watanni biyu da kwana 7 cikin iyawar Allah an sako SUMMAYA BAYAN an biya naira Miliyan 10.
In dai ba ku manta ba ranar 24 ga watan 10 ne aka yi garkuwa da Sumayya tare da su hassana da Husaina da wasu yara biyu da kuma wani matashi Mai suna SURAJO. Sai dai an sako su Hassana da Husaina Bayan an biya naira Miliyan 15 haka su. Haka daga baya aka sako su yaran kanana Bayan an biya kudin fansa. Inda aka cigaba da tsare ita Sumayya da Surajo Wanda kwanakin baya suna bayar da kwana biyu in ba a ba su abunda su ke so ba su KASHE su. Sai Allah Allah bai nufi sun kashe Sumayya ba. Sai dai ita Sumayya ta tabbatar da a gaban idanunta aka KASHE shi Surajo.

