Gwamnati tunbin giwa, ba mai iyawa da ke sai Allah. Wasu na ganin cewa muddun kana tare da gwamnati, kuna dasawa. Shi kenan Kai ka taka dahir.
Sai dai kash! Ba haka abun ya ke ba a jahar Zamfara. Hujja a nan ita ce;
A wannan duniyar ba wani Abu da ya ke muhimmanci a bangaren Jagoranci, kamar karfin kafafen yada LABARAI. Hakan ya sa kowace kasa ta ke ta kokarin Samar da kafar watsa LABARAI mai Karfi domin samun damar mulkar duniya!
Hasalima karfin kafar yada LABARAI ya fi na makamin Kare dangi....
Hakan ya sa kasashe da gwamnatocin da su ka San abunda su ke yi, sukan baiwa kafafensu muhimmanci fiye da kima.
Sai dai kash!
Ba haka abun ya ke ba a jahar Zamfara, duk da duk wani jami'in gwamnati Mai tunanen kirki da ilimin wayewar zamani ya San irin gudunmawar da kafafen Sada zumunta su ke takawa fiye da duk wata kafar watsa LABARAI mallakar jahar Zamfara, dama mazauniya jahar.
Amma ba wani tallafi na Azo a gani da ita gwamnatin ta baiwa masu taimaka mata wannan bangaren. Sai dai tarin bakin jini da bacin suna da kullum su ke tattarawa kawunansu!
Muna online tun kafin kafuwar gwamnati Mai ci a yanzu. Duk wani Wanda ya wahala a cikin wannan Gwamnatin tun 2010 zuwa yau ba daya da gwamnatin jahar ta taimaka, Hasalima wadanda su ka wahala tun farko ba daya da bai gaji ya ba baya ba. Wadanda su ka matso yanzu suna cikin wahala da ba ni hasashen za a yi masu abun da ba a yi masu baya ba.
Dan haka 'yan uwa yan soshiyal midiya, ya kamata mu yi wa kanmu kiyamullaili. Mu San Inda gari ya yi Muna Dan Hausawa sun ce da hasara gwamma, aikin kishiya.
Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau.
9-1-2019

