AN RANTSAR DA SHUWAGABANNIN KUNGIYAR DALIBBAI TA JAHAR ZAMFARA, YAU! - MAIBIREDI TV

MAIBIREDI TV

Na kirkiri wannan blog ne, domin kawo labarai na ciki da wajen Najeriya dama rubutu akan ababen da ke faruwa a jahar Zamfara.

Breaking

Home Top Ad

Responsive Ads Here

Post Top Ad

Responsive Ads Here

Saturday, 2 February 2019

AN RANTSAR DA SHUWAGABANNIN KUNGIYAR DALIBBAI TA JAHAR ZAMFARA, YAU!

Yau Assabar 2-2-2019, ne aka rantsar da shuwagabannin Kungiyar dalibbai ta jahar Zamfara.  Bikin rantsuwar Wanda ya gudana da dakin taro na JB YAKUB da ke garin Gusau.

Ya samu halartar muhimman mutane, wadanda su ka hada da 'yan siyasa, Ma'aikatan Gwamnati, shugabannin Dalibbai daga ciki da wajen Manyan makarantannin jahar Zamfara.

Barister Bashar Muhammad Maradun. Ya rantsar da dukkanin shugabannin Kungiyar farawa da Shugaban Kungiyar. Da ya ke jawabi a wajen taron. Tsohon Shugaban Kungiyar dalibbai ta jahar Comrade Mubarak Garba. Ya godewa Allah da ya ba shi damar Jagorantar Kungiyar na tsawon Shekara daya, tare da jero tarin nasarorin da su ka samu a lokacin Jagorancinsa. Inda ya roki Allah ya baiwa sabbin Jagororin ikon sauke nauyin da Aka Dora masu.

Da ya ke jawabi a wajen bikin rantsuwar, rantsattsen Shugaban Kungiyar kwamrad Ramadan Mijinyawa, ya bayyana cewa, zai yi Aiki wurjanjan domin daga martabar dalibban jahar Zamfara, ganin yadda ta tabarbare. Daga karshe Shugaban ya roki Allah ba sabbin Shugabannin ikon sauke nauyin da aka Dora masu.

Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau Zamfara (Mukaddashin Jami'in Hulda da Jama'a Na Kungiyar Dalibbai Ta Jahar Zamfara)


Post Bottom Ad

Responsive Ads Here