KWANAKI 10 KACAL NE SU KA RAGE.... - MAIBIREDI TV

MAIBIREDI TV

Na kirkiri wannan blog ne, domin kawo labarai na ciki da wajen Najeriya dama rubutu akan ababen da ke faruwa a jahar Zamfara.

Breaking

Home Top Ad

Responsive Ads Here

Post Top Ad

Responsive Ads Here

Sunday, 19 May 2019

KWANAKI 10 KACAL NE SU KA RAGE....

Yau saura kwanaki goma wannan bawan Allah, ruwa da tsakin Jagorancin zamfara ya fita daga hannunsa.

Babban rashin jin dadina da Abdulazeez Abubakar Yari bai wuce rashin Kula da sha'anin  Al'umma ba. Masifar son rai ta cika masa zuciya.

Talakan jahar ba zai taba mantawa da irin kisan kiyashi da aka yi mashi a lokacin wannan Dan tahaliki ba!

Daga nan zuwa Shekaru talatin ba za a cike gibin da wannan Dan tahaliki ya yi wa Zamfarawa ba, ta fuskar ilimi kurrum, kenan.

Ba za mu taba mantawa da irin rashin tausayin wannan Dan tahaliki ba. Domin duk Wanda za a KASHE a Zamfara ba zai damu ba, Amma Idan aka cewa za taba siyasarsa. To duniya Kaf za ta ji.

Ya Allah wannan bawan Allah in alheri, ya yi Muna Allah ka Sada shi da abunsa duniya da lahira. Allah ka yi Muna arzikin samun shuwagabannin kirki da za su yi kokarin dora jaharmu kan turba ta gari.

Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau.

19-5-2019

Post Bottom Ad

Responsive Ads Here