Taron Wanda ya gudana a dakin taro na hukumar Zakka da ke Bye Pass Gusau.
A wurin taron Dr. Mannir Bature Daga assibitin Tarayya Gusau, ya bayyana irin matsayi da yanayin mutuwar mata da kananan Yara ya ke ciki a jahar Zamfara, tare da wayarwa matan kai akan hanyoyin da ya kamata matan su bi domin inganta sha'anin kiyon lafiyarsu, tare da tabbatar da gwamnatoci sun aiwatar da kasafin kudin da su ka yi a bangaren kiyon lafiya.
Daga nan aka shiga tattaunawa tsakanin jami'an kiyon lafiya, da uwayenmu mata 'Yan siyasa. Domin ganin an samu sauyi matuka gaya a wannan bangaren domin samun sauyi don ceto mata masu juna, da yara kanana. Inda kowane bangaren ya fadi yanayin da ya ke ciki da kuma gudumawar da ya ke iya bayarwa wajen magance wadannan matsalolin.
Taron dai ya gudana ne karkashin jagorancin Alh. Abdulahi Lere mukaddashin shugabar AdvocacyNigeria tare da shugaban wannan kungiyar a jahar Zamfara. Alh. Rabiu Sambo da sauran mata 'Yan siyasa da 'Yan Gwaggwarmaya.

