WATA DAYA, DA KWANA 6 YAU KENAN, DA SAKO SAKAMAKON JARABAWAR WAEC A NAJERIYA. AMMA HAR YANZU MU TALAKAWAN JAHAR ZAMFARA MUN JI TSIT! - MAIBIREDI TV

MAIBIREDI TV

Na kirkiri wannan blog ne, domin kawo labarai na ciki da wajen Najeriya dama rubutu akan ababen da ke faruwa a jahar Zamfara.

Breaking

Home Top Ad

Responsive Ads Here

Post Top Ad

Responsive Ads Here

Thursday, 24 August 2017

WATA DAYA, DA KWANA 6 YAU KENAN, DA SAKO SAKAMAKON JARABAWAR WAEC A NAJERIYA. AMMA HAR YANZU MU TALAKAWAN JAHAR ZAMFARA MUN JI TSIT!

Mece ce makomar jarabawar ya'yan talakawan Jahar zamfara,  ya kamata gwamnati ta yi duk Mai yuyuwa Wajen ganin an kawo karshen duk wata kiki-kaka din matsalar ilimin 'ya'yan talakawan jahar zamfara.  Domin gurinmu Jaharmu ta zamo sawun gaba, amma hakan bai taba samuwa sai an inganta harkar ilmi.



Kasancewar Kusan al'ada ce, ta Gwamnatin SHEHI. Wajen Jan kafa gun biyawa 'ya'yan talakawan Jahar kudaden WAEC DA NECO a duk shekara, Wanda wannan babbar Illa ce ga duk wani Bazamfare da ke kishin kansa da Al'ummarsa. Dan Haka muna Kira ga Mai girma Gwamna ABDUL'AZIZU ABUBAKAR YARI MAFARA da Dan Allah ya ji tausayin talakawan da sunka yi masa gata....

Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau.

24-8-2017

Post Bottom Ad

Responsive Ads Here