Babban abunda ya jawo hankalin kungiyar ga shirya wannan gangamin ga dalibbai shi ne Ziyarar da Maitaimakin Shugaban kungiyar na daya Muhammad Yahaya Tambura tare wasu shuwagabannin kungiyar suka kaiwa wasu daga cikin hukumomin Tsaron Zamfara.
Da kuma wata Kasida da Shugaban kungiyar na Jaha Comr. Sen. Mubarak Garba ya Gabatar a wata tattaunawa kan matsalar tsaro da Hukumar National Institute for research and developmental studies and security agencies ta shirya a ranar 25th April 2018, a fadar Gwamnatin jahar Zamfara. Inda ya yi Karin haske akan irin gudunmawa da dalibbai za su iya bayarwa domin samar da Tsaro a jaha ba zai iya misaltuwa ba.
Taron bitar zai mayar da hankali ne, akan fadakar da Matasa Akan yada za su yaki ta'addanci a waka-junansu. Tare da dabaru da za su iya amfani da su Dan gane Dan ta'adda da dakile ta'addancin Tun kafin ya Kai ya yi Illa ga al'umma.
Bitar za ta kunshi, Kasidu daga bangarori na jami'an Tsaro, Farawa da kwamishin 'yan Sanda, darakta SSS, kwamandan Jami'an Tsaron fararen kaya (NSCDC) da sauran jami'an Tsaro da ke yaki da 'yan ta'adda. Tare da nunawa Matasa hanyoyin da za su bi domin maganin matsalar tsaro.

