A yau Talata 31-7-2018 kungiyar Muryar Talaka ta Kasa Reshen jahar Zamfara, ta kaiwa 'yan uwa 'yan gudun hijira Maza da mata da ke a karamar Hukumar Zurmi tallafin Suturu domin tallafa masu Ganin halin da 'yan gudun hijirar su ke ciki na rashin kayayyakin more rayuwa. Musamman tufafe.
Dan haka muna amfani da wannan damar mu yi kira ga kungiyoyin Kare hakkin Dan Adam, 'Yan Siyasar jahar Zamfara. Masu hannu da shuninmu da daidaikun mutane da Dan Allah mu taimaki wadannan bayin Allah.
Domin wallahi suna cikin tashin hankali marar misaltuwa.
Allah ya sa a dace amin.
Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau Pro 1 Muryar Talaka Reshen jahar Zamfara.
31-7-2018

