Daya daga cikin jagororin Matasan jahar Zamfara, Shugaban kungiyar labour room Global initiative. His excellency Governor Labour Room Zamfara State AMB. Nura Isah Gusau. Ya yi kira ga al'ummar jahar Zamfara. Da su fito kwansu da kwarkwatarsu su zabi jagoran da su ke so ya jagorance su.
Matashin ya kara da Kira ga al'ummar jahar Zamfara da su tabbatar sun bi doka da oda wajen yin wannan zaben domin tabbatar da an yi zaben Lafiya an Kammala Lafiya.
Daga karshe ya roki Allah ya sa a yi wannan zaben Lafiya a Kammala Lafiya. Haka zalika ya roki Allah ya baiwa jahar Zamfara jagora adili wanda zai jagoranci bunkasar tattalin arziki da cigaban jahar Zamfara baki daya

