A cigaba Da yunkurinsa na daga martabar jahar Zamfara. Tare da samar da zaman lafiya a jahar ta yadda kowa zai zauna a cikin aminci.
Mai girma gwamnan jahar Zamfara Bello Matawalle duk da yana cigaba da ibadar umara yanzu haka. Haka bai hana shi aiki tukuru ba, wajen samun nasarar ceto rayuwar Dan uwan sanannen Dan siyasar nan Dr. Dauda Lawal Dare wato Yusuf Lawal Dare.
Yusuf Dai an yi garkuwa Da shi ne watanni uku da su ka wuce baya. Wanda masu garkuwan su ka nemi sai an biya naira miliyan dari UKU (N300,000000) kudin fansa Kafin su sake shi. Sai dai bayan zamansa gwamna ta amfani Da kwararru tare kwarewar gwamnan a matsayin tsohon shugaban kwamitin tsaro da asiri na majalissar wakilai ta kasa. an yi nasarar sako shi. Talata
Gwamna matawalle ya bayar da tabbacin gwamnatinsa. Za ta tashi tsaye wajen Kare rayukka da dukiyoyin al'ummar jahar Zamfara.
- Ibrahim Bello Zauma
SSA (New Media)
Fassara: Abdulmalik Saidu Mai Biredi Tashar Bagu Gusau

