GWAMNATIN ZAMFARA TA TALLAFAWA IYALAN TSOFAFFIN SOJOJI, ALBARKACIN RANAR 'YAN MAZAN-JIYAN. - MAIBIREDI TV

MAIBIREDI TV

Na kirkiri wannan blog ne, domin kawo labarai na ciki da wajen Najeriya dama rubutu akan ababen da ke faruwa a jahar Zamfara.

Breaking

Home Top Ad

Responsive Ads Here

Post Top Ad

Responsive Ads Here

Wednesday, 15 January 2020

GWAMNATIN ZAMFARA TA TALLAFAWA IYALAN TSOFAFFIN SOJOJI, ALBARKACIN RANAR 'YAN MAZAN-JIYAN.

A Cigaba da yunkurinta na bunkasa walwala da jin dadin Al'ummarta. Gwamnatin jahar Zamfara karkashin jagorancin Hon Dr Bello Muhammad Matawallen Maradun, ta bayar da tallafin kudi, Buhuhuwan Hatsi da shanu ga tsofafin Sojojin da su ka sadaukar da rayuwarsu don daurewar kasar nan da kwanciyar hankalin al'ummarta.

Da ya ke jawabi Mai Daraja Gwamnan jahar Zamfara Wanda Sakataren gwamnatin Hon. Bala Bello Maru ya wakilta, ya bayyana cewa: "Shakka babu wadannan bayin Allah sun sadaukar da kurciyarsu. Domin daurewar kasar nan. Wanda har Allah ya nufi su ka Kai shekarun Ajiye aiki.

"Don haka ya zama dole ga gwamnatinmu ta yi duk Mai yuyuwa wajen kyautata jin dadi da walwalar wadanann bayin Allah. Wanda haka ya sa mu ka ware wadannan kudi, abinci da kuma wadannan shanun domin tallafawa wadannan mazaje.

Ranar 15 Junairu dai ta kowace shekara Rana ce da ake bikin 'Yan Mazan-jiya a Nigeria. Akan ware ranar ne domin kyautata jin dadi da walwalar tsofafin sojojin da su ka baitawa Kasa tare da kokarin tallafa masu.

 Abdulmalik Saidu maibiredi
Senior Special Assistant to the Governor Of Zamfara State.
15th January, 2020

Post Bottom Ad

Responsive Ads Here