A Cigaba karbar tallafi domin shirin KO-TA-KWANA kan annobar Coronavirus a jahar Zamfara, Kungiyar Kwamishinonin jahar Zamfara karkashin Kwamishinan Shari'a, Hon. Barista Nura Ibrahim Zarumi tare da Exco dinsa da ma'aji Ibrahim Jibo Magayakin Kaura. Da Pro Hon. Sulaiman Anka da shugaban Kwamitin jin dadi da walwala Hon. Muhammad Maiturare, Bungudu. Sun ba da tallafin Naira Miliyan biyar ga Kwamitin KO-TA-KWANA kan annobar Coronavirus. Domin tallafawa Al'ummar jahar domin yakar annobar Coronavirus, da su ke bayar da tallafin Kwamishinonan sun bayyana cewa wannan na daga cikin gudunmawarsu ganin sun inganta Walwala da jin dadin Al'umma jahar Zamfara.
Da ya ke Mayar da jawabi shugaban Kwamitin KO-TA-KWANA kan annobar Coronavirus kuma Kakakin majalissar dokokin jahar Zamfara Rt. Hon. Nasiru Mu'azu Magarya. Ya bayyana matukar jin dadinsa da wannan tallafi da wadannan Kwamishinonin su ka bayar, ya kuma yi alkawarin yin amfani da kudin domin tallafawa talakawan jahar Zamfara. Haka Zalika ya yi kira ga sauran masu hannu-da-shuninmu a jahar Zamfara da sauran Yan siyasa da su tashi tsaye wajen tallafawa talakawa.
Abdulmalik Saidu Maibiredi
Senior Special Assistant to the Governor Of Zamfara State
17/4/2020







